Tsohon shugaban Kasa kuma shugaban kwamitin sasanta tsohon Sarkin Kano Sanusi da Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Ganduje, Abdussalami Abubakar ya bayyana cewa lallai da a ce Buhari ya duba shawarwarin da suka bada a rahoton su da yana ganin ba zai kai ga tsige sarki Sanusi ba.